https://nounrespectively.com/99/54/39/995439caf4e551e612393deb186603a4.js'

Shugaban Hukumar Tace Fina-finai ta Kano Malam Abba Almustapha ya yiwa Freedom Radio karin bayani kan dalilansu na dakatar da Jaruma Khadija Mai Numfashi daga Kannywood har tsahon shekaru biyu.

Assalamu alaikum wato bidiyo ne ya yadu/bazu yadda suke zuwa suna raye raye na rashin kamun kai , na tozarci wanda babu daɗi kuma kowa yasan irin yadda korafe korafen da muke karba a koda yaushe mun kirata domin ta kare kanta, ya akayi tabari tana yar masana’atar kannywood da ake bata tarbiyya kada ta yarda tana irin wadannan abubuwan da zasu iya jawo cece kuce. 

Wanda zai iya zamo illa ga al’ummar jihar kano, ko kuma makalla tanmu na shirye shiryen mu kada mu saka kanmu irin wadannan raye raye amma ta saki wannan bidiyo na gidan rawa, mun kirata domin muji daga gareta abun ya faskara.

Babban laifin da zakayiwa hukumar mu ,mu kiraka ka kasa gayyatarmu- inji abba almustapha.

Mun kirawo ta tace bata gari yaushe zaki dawo garin , ta dawo garin mun san tana garin tazo koda mu samu sasauci ne muji daga gareta koda mu tsawatar mata taki ta bari.

Saboda haka wannan shine hukuncin da muka dauka a yanzu bara mugani zuwa nan gaba”- inji abba almustapha. 

Related Post

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *